Home Labarai Gwamnatin tarayya ta kara ranar Alhamis matsayin ranar hutun sallah

Gwamnatin tarayya ta kara ranar Alhamis matsayin ranar hutun sallah

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta ayyana ranar Alhamis 11 ga watan Afrilu, 2024 matsayin Kari cikin ranakun hutu a kasar, a wani bangare na bukukuwan karamar sallah ta shekarar 1445 bayan hijra.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakatariyar ma’aikatar cikin gida Dr. Aishetu Gogo Ndayako.

Sanarwar ta ambaci ministan ma’aikatar Dr. Olubunmi Tunji-Ojo, na taya daukacin Al’ummar Musulmin kasar murnar kamala ibadar azumin watan Ramadan cikin kwanciyar hankali, inda kuma ya bayyana kudirin shugaban kasar Bola Ahmad Tinubu na samawa ‘yan kasar kyakkyawan yanayi.

Idan zamu iya tunawa jaridar PRNigeria ta ambaci ministan ya ayyana ranar talata 9 da kuma 10 ga watan Afrilun, 2024 matsayin ranakun hutun karamar a kasar.

 PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp