Home Labarai Kotu ta tabbatar da dakatar da Ganduje daga APC

Kotu ta tabbatar da dakatar da Ganduje daga APC

Wata babbar kotu a jihar Kano ta tabbatar da dakatarwar da aka yi wa shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje.

Idan dai za’a iya tunawa kwanaki biyu da suka gabata ne shugabancin APC na mazabar Ganduje a Karamar Hukumar Dawakin Tofa, mahaifar Ganduje, ya dakatar da shi bisa zargin cin-hanci da rashawa da gwamnatin Kano ke yi masa.

Ta cikin umarnin kotun, ƙarƙashin Mai Shari’a Usman Na’abba, ta hana Ganduje, wanda shine tsohon gwamnan Kano, nuna kan sa a matsayin shugaban jam’iyyar APC.

Na’abba ya kuma hana Ganduje yin wani taro ko daukar mataki a matsayin shugaban jam’iyyar har sai an kammala zaman sauraron karar.

Ya kuma hana shugabancin jam’iyyar na jiha shiga cikin maganar da take gaban kotu.

Dr. Ibrahim Sa’ad, a madadin biyu daga cikin shugabannin APC na mazabar Ganduje, mataimakin sakatare, Laminu Sani da mai baiwa jam’iyyar shawara kan harkokin Shari’a, Haladu Gwanjo ne ya shigar da karar.

Haka kuma kotun ta umarci waɗanda ake kara su hudu da suka haɗa da jam’iyar APC a matakin kasa da jiha da kuma shi Ganduje din da su tsaya a matsayin su daga 15 ga Afrilu zuwa 30 ga watan Afrilu lokacin da za a saurari karar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp