Home Labarai An janye ‘yan sandan dake gadin Yahaya Bello

An janye ‘yan sandan dake gadin Yahaya Bello

Babban Sufeto ‘yan sandan Najeriya IGP Olukayode Egbetokun, ya bayar da umarnin janye dukkan jami’an ‘yan sandan da ke gadin tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello.

Wannan na kunshe ta cikin wata takar da mai dauke da adireshin hedkwatar ‘yan sandan Najeriya da aka aika zuwa MOPL 37 a Lokoja.

Takardar mai lamba: “CB:4001/DOPS/PMF/FHQ/ABJ/VOL.48/34 ta bayyana cewa, “babban Sefeton ‘yan sandan Nijeriya ya ba da umarnin janye dukkan ‘yan sandan da ke raka tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Alhaji Yahaya Bello.

Idan za’a iya tunawa a ranar Alhamis din da ta gabata ne Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), a wata takarda da ta fitar ta sanya tsohon Gwamnan cikin jerin sunayen wadanda zasu fara farauta.

Wannan dai ya biyo bayan rashin nasarar da hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC ta yi na kama Yahaya Bello a gidansa da ke Abuja, sakamakon zarginsa da ake da karkatar da kudade har N80.2billion.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp