Home Labarai Rundunar Sojojin Nijeriya zata hukunta sojojin da suka hari a Tudun Biri

Rundunar Sojojin Nijeriya zata hukunta sojojin da suka hari a Tudun Biri

Shalkwatar tsaron Nijeriya ta ce sojojin da aka samu da laifi a kai hari kan masu mauludi a kauyen tudun biri na Jihar Kaduna zasu gurfana a gaban kotun hukunta sojoji domin fuskantar hukunci.

Daraktan yaɗa labarai na hedikwatar tsaron, Edward Buba ne ya bayyana haka a taron yaɗa labaran da aka gudanar a Abuja.

inda yace Hedikwatar tsaron ta kammala binciken da aka daɗe ana dako kan bam ɗin da aka jefa kan mutane a ƙauyen Tudun Biri dake a ƙaramar hukumar Igabi da ke jihar Kaduna.

A Disambar bara ne wani jirgin sojoji ya jefa bam kan mutanen da ke bikin maulidi lamarin da ya janyo asarar rayuka da jikkatar wasu da dama.

Rundunar sojin Najeriya ta ɗauki alhakin kai harin inda ta ce lamarin ya faru bisa kuskure.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp