Home Labarai Sojoji sun gano haramtattun matatun mai 50 a Neja Delta

Sojoji sun gano haramtattun matatun mai 50 a Neja Delta

Rundunar sojin Najeriya ta bankaɗo haramtattun matatun mai 50 a dajin Biseni da ke ƙaramar hukumar Yenagoa a jihar Bayelsa, a yankin Neja Delta mai arzikin man.

Kwamandan rundunar haɗin gwiwa ta Operation Delta Safe a yankin, Rear Admiral John Okeke wanda kuma ya jagoranci samamen ne ya bayyana haka.

Okeke a yayin da yake magana da ƴan jarida ya ce a ranar 9 ga watan Mayu, sun kai samame ƙaramar hukumar Ukwa ta Yamma da ke jihar Abia kan iyaka da Rivers, ya kuma ce za su ci gaba da kai irin wannan samame domin gano wasu matatun mai da ake gudanar da su ba bisa ƙa’ida ba.

A cewarsa, sun gano wani rami da aka haƙa a ɗaya daga cikin haramtattun matatar mai wanda ke iya ɗaukan manyan motoci 10 maƙare da duro-duro na iskar gas inda kuma suke ajiye ɗanyan mai wanda daga nan kuma su riƙa shigar da shi wurin girke-girkensu.

Rear Admiral John Okeke ya ƙara da cewa za su ci gaba da kai irin wannan samame domin fatattakar masu fasa-ƙwabrin mai a yankin na Neja Delta.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp