Home General Kungiyoyin a Nijeriya Kwadago sun fara yajin aiki a ranar litinin

Kungiyoyin a Nijeriya Kwadago sun fara yajin aiki a ranar litinin

An wayi gari da yakin aikin kungiyoyin kwadago a Nijeriya abin da ake tsammanin Akwai yiyuwar ayyukan tattalin arziki a kasar su tsaya cik sanadin yajin aikin.

Kokarin da shuwagabannin Majalisar dokokin kasar suka yi domin sasanta bangarorin ya ci-tura.

Bayan ganawar sa’o’i hudu da shugabannin Majalisar dokokin kasar da yammacin ranar Lahadi a Abuja, shugabannin kungiyar kwadagon sun ce babu gudu babu ja da baya game da yajin aikin gama gari da aka shirya ya fara ranar Litinin 3 ga watan Yuni, 2024.

Sai dai shugaban kungiyar kwadago ta TUC, Festus Osifo ya ce za su tunbi sauran reshoshinsu a kan kiran da shugabannin Majalisar suka yi mu su ma a kan su janye yajin aikin.

“A yanzu ba mu da hurumin janye yajin aikin, yajin aikin zai fara ne yayin da mu mika rokon da shugabbanin Majalisar dokokin kasar suka yi ga rassan mu daban-daban, game da kiran da suka yi a kan mu janye yajin aikin” inji shi.

Tun da farko, Osifo, shugaban kungiyar kwadago (TUC); da takwaransa na kungiyar kwadago ta Najeriya (NLC), Joe Ajaero; sun gana da shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio da kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas. a Abuja.

Kungiyoyin kwadagon sun kira yajin aikin ne sakamakon rashin cimma matsaya a tattaunwar da bangarorin biyu ke yi da gwamnatin kasar kan sabon mafi karancin albashin ma’aikata.

Kungiyoyin kwadago fiye da 10 sun yi kira ga ma’aikatansu da su amsa kiran uwar kungiyar kwadago ta kasa har sai abinda hali ya yi.

Ma’aikatan lafiya da bankunan kasuwanci da na sufurin jiragen sama da na sauran fanonin na cikin wadanda za su shiga yajin aiki, abinda ake ganin zai kawo nakasu ga tattalin arzikin kasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp