Home General Hukumar ‘Yan Sanda tace baza ta bi Umarnin Gwamnatin Kano ba.

Hukumar ‘Yan Sanda tace baza ta bi Umarnin Gwamnatin Kano ba.

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta bayyana umarnin ta na bijerewa umarnin gwamnan jihar na fidda tsohon sarkin kano Aminu Ado Bayero daga Gidan sarki na Nassarawa.

Idan za’a iya tunawa a ranar Alhamis gwamnan jihar Kano ta bakin kwamishinan Shari’a na jihar Haruna Dederi ya bawa kwamishinan ‘yan sandan jihar Usaini Gumel kan ya fidda tsohon sarkin daga gidan bisa hukuncin kotu tarayya dake jihar kano da ya tabbatar da dokar da majalisar jihar kano ta samar a 2024.

Da ya ke ganawa ta wayar tarho da wakilin jaridar Punch a ranar Juma’a, kwamishinan ‘yan sandan yace bin umarnin gwamnan na fitar da tsohon sarkin tamkar riga malam masallaci ne.

Yace gwamnatin dai da ta bayar da umarnin itace ta shigar da kara gaba gaban babbar kotun jiha akan batun na fitar da sarkin wanda ktoun zata zauna a ranar litinin 24 Yuni 2024.

Tun bayan umarnin gwamantin jihar ta Kano, aka wayi gari da sake girke jami’an ‘yan sanda a harabar gidan sarkin na Nassarawa, inda tsohon sarkin kano Aminu Ado Bayero yace Gwamnatin jihar na tsrae da shi a ciki.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp