Hukumar ‘Yan Sanda tace baza ta bi Umarnin Gwamnatin Kano ba.

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta bayyana umarnin ta na bijerewa umarnin gwamnan jihar na fidda tsohon sarkin kano Aminu Ado Bayero daga Gidan sarki na Nassarawa.

Idan za’a iya tunawa a ranar Alhamis gwamnan jihar Kano ta bakin kwamishinan Shari’a na jihar Haruna Dederi ya bawa kwamishinan ‘yan sandan jihar Usaini Gumel kan ya fidda tsohon sarkin daga gidan bisa hukuncin kotu tarayya dake jihar kano da ya tabbatar da dokar da majalisar jihar kano ta samar a 2024.

Da ya ke ganawa ta wayar tarho da wakilin jaridar Punch a ranar Juma’a, kwamishinan ‘yan sandan yace bin umarnin gwamnan na fitar da tsohon sarkin tamkar riga malam masallaci ne.

Yace gwamnatin dai da ta bayar da umarnin itace ta shigar da kara gaba gaban babbar kotun jiha akan batun na fitar da sarkin wanda ktoun zata zauna a ranar litinin 24 Yuni 2024.

Tun bayan umarnin gwamantin jihar ta Kano, aka wayi gari da sake girke jami’an ‘yan sanda a harabar gidan sarkin na Nassarawa, inda tsohon sarkin kano Aminu Ado Bayero yace Gwamnatin jihar na tsrae da shi a ciki.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 24 minutes 5 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 5 minutes 30 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com