Home General Sojojin Nijeriya sun kashe dan fashin daji Alhaji Kachalla Ragas a jihar...

Sojojin Nijeriya sun kashe dan fashin daji Alhaji Kachalla Ragas a jihar Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta ce jami’an tsaron haɗin gwiwa sun kashe wani jagoran ‘yan fashin daji mai suna Alhaji Kachalla Ragas tare da wasu abokan harkarsa da dama.

Wata sanarwa da Kwamashinan Tsaron jihar Samuel Aruwan ya fitar a yau Juma’a ta ce dakarun rundunar Operation Whirl Punch ne suka yi nasarar kashe shi bayan hare-haren da suka kai ta sama a ƙaramar hukumar Giwa da ke jihar ta arewa maso yammacin Najeriya.

“Hare-haren ta sama da ƙasa sun yi nasarar kashe ‘yanbindiga da yawa tare da shugabanninsu a dajin Yadi da ke yankin Bula,” in ji sanarwar.

Ya ƙara da cewa an kai harin ne bayan samun bayanan sirri cewa ‘yanbindigar “za su yi wani taro don kitsa mummunan aiki, inda daga baya masu leƙen asiri suka hangi gungun mutum bakwai zuwa 10 ɗauke da makamai”.

“Cikin waɗanda aka kashe har da Alhaji Kachalla Ragas, wanda abokin Buharin Yadi ne wanda shi ma aka kashe kwanan nan,” a cewar sanarwar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp