Sojojin saman Nijeriya sun hallaka Mayakan Boko Haram 7 a Jihar Borno

Sojojin saman Nijeriya dake karkashin Operation Hadin kai sun sami nasarar hallaka ýan Ta’adda 7 a jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya.

wanna na cikin wata sanrwa da darakta yada labarai da hulda da jama’a na rundunar AVM Edward Gabkwet ya fitar ranar alhamisa a birnin tarayya Abuja.

Gabkwet ta cikin sanarwar yace dakarun sun sami nasarar ne bayan farwa maboyar ‘yan ta’addan dake tsaunikan Degbewa da Chinene dukkan su a Mandara.

Ya kara da cewa kafin dakarun sojin saman su kai harin sai da suka gudanar bincike gami da sintiri a yankunan na tsahon kwanaki, wanda ya hadar da tantance adadin ‘yan ta’addan dake rayuwa a wurin.

Ya kuma ce ana zargin wajen matsayin wani wuri na hada abubuwan fashe da killace su.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1187 days 12 hours 56 minutes 25 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1169 days 14 hours 37 minutes 50 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com