Home DUNIYA NSA ta mika mutum 16 da aka kubutar da hanun ‘yan Ta’adda...

NSA ta mika mutum 16 da aka kubutar da hanun ‘yan Ta’adda ga Gwamnatin Zamfara

Babban ma shawarcin shugaban kasa kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu, ya hannunta mutane 16 da aka kubutar daga hannun masu garkuwa da mutane ga wakilan gwamnatin jihar Zamfara.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da shugaban sashen sadarwa da dabaru na cibiyar yaki da ýan ta’adda a ofishin mai babban mai shawarcin , NCTC – ONSA, a ranar alhamis a birnin tarayya Abuja.

Ribadu yace damka wadanda aka kubutar din na shaida kan yunkurin gwamnatin tarayya kan mabanbanta ceto wadanda masu garkuwa da mutane suka kama sannan ya nuna kokarin gwamnatin tarayyar Nijeriya na kare rayukan ýan Nijeriya da wadanda ke tsare a hannun masu garkuwa da mutane.

Yace an yi garkuwa da mutanen ne a kwaryar Zurmi, Duran da Gusau dake cikin garin Zamfara a ranar 22 ga watan Afrilu, wanda kuma atisayen da NCTC ya sami nasarar kubutar da su.

Ya bukaci al’umma Nijeirya da su cigaba da bawa jamián tsaro goyan baya domin cimma kudirin gwamnatin tarayya na kawar matsalolin tsaro a Nijeriya.

daga bisani kodinatan NTCT, Manjo Janar Adamu Laka ya bukaci al’umma dasu ke gaggauta sanar da Jami’an tsaro da zarar wani lamarin tsaro ya auku domin daukar mataki da wuri.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp