Home DUNIYA Rumbun wutar lantarkin Najeriya ya sake ɗaukewa a karo na 4 cikin...

Rumbun wutar lantarkin Najeriya ya sake ɗaukewa a karo na 4 cikin 2024

Kamfanin Dakon Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya tabbatar da sake ɗaukewar wutar lantarki daga rumbun samar da ita na Najeriya a ranar Asabar.

Wannan dai shi ne karo na huɗu da wutar ta ke ɗaukewa gaba ɗaya tun daga farkon wannan shekarar zuwa yanzu.

Wani rahoto da kamfanin ya wallafa a shafinsa na internet ya nuna cewa da misalin karfe 2:00 na yammacin wannan rana an iya samar da wutar da yawanta ya kai megawat 2,797.16, kasa da yadda ake samu a baya, idan an kwatanta da misalin karfe 1:00 na wannan yammaci da ya kai megawatt 3,417.99.

Haka adadin wutar ya sake saka da misalign karfe 3 na yammacin zuwa 1,020.08 inda daga bisani cikin mamaki ya koma 0.80 da karfe.

Ba tun yanzu ba ’yan Najeriya ke kokawa kan yadda rashin wutar lantarki ke haifar musu da tasgaro a harkokin su na yau da kullum.

A bana kaɗai, kasar nan ta fuskanci durkushewar wutar lantarki akalla sau uku, inda matsalar ta faru sau 227 a tsahon shekaru 14 kamar yadda kamfanin dakon wutar lantarkin na TCN ya bayyana.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp