Kada ku bari ’yan ta’adda su kassara zaman lafiyar kasar nan – Tinubu ga sojoji

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bukaci dakarun sojoji da kada su bari ’yan ta’adda su ga bayan al’ummar Nijeriya.

Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Asabar a wani bangare na bikin da rundunar sojin ta gudanar a barikin sojoji na uku da ke Rukuba a Karamar Hukumar Bassa a jihar Filato.

Tinubu wanda ya sami wakilcin Ministan Tsaro, Alhaji Badaru Abubakar, ya ce wajibi dakarun su kare rayukan ’yan kasar a gidaje ko kuma a wuraren mu’amalarsu na yau da kullum.

da yake bayani tun da farko, Babban Hafsan Sojojin Nijeriya, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja, ya ce sojojin kasar nan kwararru ne tsahon shekaru 161.

Nijeriya dai na fama da matsalolin rashin tsaro wacce ta addabi Arewacin kasar, yayin da na kudanci ke fama da matsaloli barayin mai da masu kokarin ficewa daga ƙasar.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 7 hours 57 minutes 43 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 9 hours 39 minutes 8 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com