Home DUNIYA Dalilin Gwamnatin Nijeriya na dakadar da biyan haraji kan kayan Abinci

Dalilin Gwamnatin Nijeriya na dakadar da biyan haraji kan kayan Abinci

Gwamnatin Nijeriya ta cire harajin da dukkannin wasu kunji-kunji kan kayan kayan abincin da zaá shigo da su kasar.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da ministan noma da samar da wadataccen abinci Abubakar Kyari ya sanyawa hannun a ranar litinin.

abincin da sanarwar ta lisafta sun hadar da samfarerar shinkafa, masara, alkama da kuma tsabar wake.

yace dakatar da biyan harajin na matsayin wani mataki cikin matakan da gwamnati zata dauka nan da kanaki 180 masu zuwa na kawar da matsalar tsadar abinci a kasar.

Ya ce shugaba Tinubu ya amince da janye kudin fito kan muhimman kayan abincin ne har tsawon kwanaki 150, domin saukaka tsadar kayayyakin abinci da ake fama da su.

Ministan, ya bayyana irin ƙoƙarin da Gwamnatin Tarayya ke yi na yaƙi da hauhawar farashin kayan abinci.

Tsada da matsin rayuwa ya ƙaru tun bayan da Shugaba Tinubu ya hau kan karagar mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Gwamnati za ta shigo da alkama da masara daga waje, Sanarwar ta ce baya ga janye ƙuɗin fito ga ’yan kasuwa masu buƙatar shigo da kayan abinci.

Har wa yau, Gwamnatin Tarayya za ta shigo da alkama kimanin tan dubu 250 da masara tan 250 da za ta bai wa kamfanoni jihohi da ke sarrafa su.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp