Home DUNIYA Dalilin Gwamnatin Nijeriya na dakadar da biyan haraji kan kayan Abinci

Dalilin Gwamnatin Nijeriya na dakadar da biyan haraji kan kayan Abinci

Gwamnatin Nijeriya ta cire harajin da dukkannin wasu kunji-kunji kan kayan kayan abincin da zaá shigo da su kasar.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da ministan noma da samar da wadataccen abinci Abubakar Kyari ya sanyawa hannun a ranar litinin.

abincin da sanarwar ta lisafta sun hadar da samfarerar shinkafa, masara, alkama da kuma tsabar wake.

yace dakatar da biyan harajin na matsayin wani mataki cikin matakan da gwamnati zata dauka nan da kanaki 180 masu zuwa na kawar da matsalar tsadar abinci a kasar.

Ya ce shugaba Tinubu ya amince da janye kudin fito kan muhimman kayan abincin ne har tsawon kwanaki 150, domin saukaka tsadar kayayyakin abinci da ake fama da su.

Ministan, ya bayyana irin ƙoƙarin da Gwamnatin Tarayya ke yi na yaƙi da hauhawar farashin kayan abinci.

Tsada da matsin rayuwa ya ƙaru tun bayan da Shugaba Tinubu ya hau kan karagar mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Gwamnati za ta shigo da alkama da masara daga waje, Sanarwar ta ce baya ga janye ƙuɗin fito ga ’yan kasuwa masu buƙatar shigo da kayan abinci.

Har wa yau, Gwamnatin Tarayya za ta shigo da alkama kimanin tan dubu 250 da masara tan 250 da za ta bai wa kamfanoni jihohi da ke sarrafa su.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp