Majalisar wakilai ta bukaci a gaggauta dakarar da yarjejeniyar Samoa

Majalisar Wakilan Nijeriya ta bukaci gwamnatin Tarayya ta yi gaggawar dakatar da yarjejeniyar SAMOA da ta haifar da cece-kuce da zargin taba martabar addini da al’adun mutanen Nijeriya.

Majalisar ta kuma yanke shawarar bincikar yarjejeniyar da gwamnatin tarayya ta rattabawa hannu a ranar 28 ga watan Yuni.

An zartar da kudurin ne biyo bayan amincewa da kudirin gaggawa na Ali Sani Madaki,  sashin  marasa rinjaye, da wasu ‘yan majalisa 87 suka dauki nauyi.

Kwanan nan yarjejeniyar ta haifar da cece-kuce saboda rahotannin cewa an shigar da tanade-tanade da suka shafi ‘yan madigo, ‘yan luwadi, bisexual, da transgender (LGBT) a cikin yarjejeniyar.

sai dai wannan na zuwa ne daidai lokacin da kungiyar lauyoyin kasar ta NBA da ake kallon matsayin masana doka suka fitar da sanarwar dake cewa cikin yarjejeniyar babu wani batun auren jinsi ko makamantan sa.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1188 days 1 hour 54 minutes 35 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1170 days 3 hours 36 minutes 0 second

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com