Home DUNIYA Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ba zata lamunci ayyukan garkuwa...

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ba zata lamunci ayyukan garkuwa a jihar ba

Rundunar ‘Yan sandan jihar Kano ta sami nasarar ceto wata ƙaramar yarinya mai kimanin shekara biyu da rabi, bayan wani Makocinsu yayi garkuwa da ita harya nemi kuɗin fansar Naira Miliyan 2 a wurin iyayenta.
wannan na kunshe ta cikin wata sanarwar da Jami’in hulda da Jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, inda tace, tuni wanda ake zargin ya amsa laifin sa harma ya kai Jami’an rundunar wurin da ya ɓoye yarinyar.
Lamarin ya faru ne unguwar Sabuwar Gandu Kwarin Barka dake ƙaramar hukumar Kumbotso, inda matashin me suna Zakariyya Muhammad ɗan kimanin Shekaru 22 ya sace yarinyar me suna Amina.
Haka kuma rundunar ta kai yarinyar Asibitin ƙwararru na Murtala Muhammed dake Kano, inda aka bata kulawar gaggawa wanda tuni aka sallame ta.
Kwamishinan ‘yansandan jihar CP Salman Dogo Garba ya ce rundunar ba zata lamunci irin waɗannan ayyukan ba, a inda ya jaddada cewa zasu saka ƙafar wando ɗaya da masu yunƙurin aikata muggan laifuka a jihar.
daga bisani rundunar ta yaba da yadda al’ummar jihar suke bin doka da oda, harma ta buƙaci mutane su ci-gaba da sanya idanu a yankunan su domin bada gudunmawar kakkaɓe dukkan wasu ɓata gari a fadin jihar.
PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp