Home DUNIYA Kamfanonin jaragen Sama da ke saba ka’idoji za su fuskanci hukunci mai...

Kamfanonin jaragen Sama da ke saba ka’idoji za su fuskanci hukunci mai tsanani – NCAA

Hukumar kula da sufurin jiragen sama ta Najeriya, NCAA ta yi gargaɗin cewa za ta hukunta kamfanonin sufurin da ke yaudarar matafiya a kan lokacin tafiyar jirage.

Mukaddashin daraktan hukumar, Chris Najomo ne ya bayyana hakan inda ya ce hukumar ba za ta lamunci rashin cika alƙawari da kuma kiyaye ƙa’idojin sufurin jirgin sama ba.

Ya yi gargaɗin cewa kamfanonin da suke saba ka’idojin za su fuskanci hukunci mai tsanani, kamar yadda doka ta yi tanadi.

Hukumar ta ce ta yi tanadi mai inganci domin sauƙaƙe yadda ake mallakar lasisin gudanar da kamfanonin jiragen sama a Najeriya, da kuma kaucewa kura-kuran baya.

“NCAA ta na fatan ganin hakan zai sa kamfanonin jiragen su tashi tsaye domin gudanar da ayyukan su yadda ya dace” inji Chris Najomo.

NCAA ta jaddada cewa babu wani dalili da zai hana kamfanonin jiragen sama gudanar da ayyukan cikin tsari kamar yadda ake yi a sauran ƙasashen duniya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp