Yadda Gwamnatin Jihar Borno ta karbi Tubabbun ‘Yan Boko Haram 8,490 a jihar

Gwamnatin Jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya ta ce ta sami nasarar karbar tubabbun mayakan kungiyar boko haram 8,490 ta hanya shirin sabunta jihar Borno wato  (Borno modern).

Kwamishinan yada labaran jihar farfesa Usman Tar ne ya bayyana hakan yayin da ake bawa tubabbun mayakan 560 rantsuwar tuba a birnin maiduguri a ranar laraba.

yace wannan sanannen al’mari ne ga dakarun sojojin da sauran jami’an tsaro dama masu rike da sarautun gargajiya a jihar.

yace shirin na tafiya yadda yakamata sannan kuma sun kama kwamiti domin bindiddigi, inda ya tabbatar da cewa wadanda suka tuban basa sake  komawa ruwa tare da karya dokoki, sai dai suna komawa harkokin su na kasuwanci ne ma.

shima da yake jawabi a yayin  taron mashawarci na musamman kan harkokin tsaro ga Gwamnan Jihar Birgediya Janar Abdullahi Ishaq (mai ritaya), ya tabbatar da adadin inda yace zuwa yanzu gwamantin jihar ta sami nasarar karbar tubabbun mayakan da suka kai 8,490, wanda hakan ya rage hadarin da al’ummar jihar ke fuskanta.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 20 minutes 38 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 2 minutes 3 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com