Home General Yadda Gwamnatin Jihar Borno ta karbi Tubabbun ‘Yan Boko Haram 8,490 a...

Yadda Gwamnatin Jihar Borno ta karbi Tubabbun ‘Yan Boko Haram 8,490 a jihar

Gwamnatin Jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya ta ce ta sami nasarar karbar tubabbun mayakan kungiyar boko haram 8,490 ta hanya shirin sabunta jihar Borno wato  (Borno modern).

Kwamishinan yada labaran jihar farfesa Usman Tar ne ya bayyana hakan yayin da ake bawa tubabbun mayakan 560 rantsuwar tuba a birnin maiduguri a ranar laraba.

yace wannan sanannen al’mari ne ga dakarun sojojin da sauran jami’an tsaro dama masu rike da sarautun gargajiya a jihar.

yace shirin na tafiya yadda yakamata sannan kuma sun kama kwamiti domin bindiddigi, inda ya tabbatar da cewa wadanda suka tuban basa sake  komawa ruwa tare da karya dokoki, sai dai suna komawa harkokin su na kasuwanci ne ma.

shima da yake jawabi a yayin  taron mashawarci na musamman kan harkokin tsaro ga Gwamnan Jihar Birgediya Janar Abdullahi Ishaq (mai ritaya), ya tabbatar da adadin inda yace zuwa yanzu gwamantin jihar ta sami nasarar karbar tubabbun mayakan da suka kai 8,490, wanda hakan ya rage hadarin da al’ummar jihar ke fuskanta.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp