Ba zamu saci kudin ku ba, ba zamu bari a sata ba – Gwamnan Kano

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa bazai saci dukiyar Al’ummar jihar kano ba, kuma bazai bari a satar musu kudi ba.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yammacin asabar yayin da yake kaddamar da kasha na biyu na rabon tallafi ga Al’ummar kananan hukumomi 44 dake fadin jihar nan.

Abba ya bayyana cewa gwamnatinsa baza ta saci kudin al’ummar jihar ba, sannan kuma zata dauki matakin hukunta dukkan wanda ya saci kudin a karkashin kulawarsa.

Gwamnan yace zasu raba miliyan 260 ga mata 5,200 wadanda suka fito daga kananan hukumomin jihar 44, wanda kowacce zata sami naira dubu 50, wanda zai taimakesu wajen sanya jari.

Haka kuma yace zasu cigaba da taimakawa matan dake kananan hukumomin da naira miliyan 260 a dukkanin wata har zuwa karshen wa’adin mulkin sa.

Yace wannan na cikin kudirin su da kuma abinda suka yi al’ummar jihar alkawari a yayin yakin neman zabe, kuma wannan na matsayin sakayya da zasu yiwa mata bisa gudunmawar da suka bayar wajen kafa gwamnatin.

PRNigeria hausa

 

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 13 hours 42 minutes 52 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 15 hours 24 minutes 17 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com