Home General Kudurin kirkirar sarakuna 3 masu daraja ta 2 ya tsallake karatu a...

Kudurin kirkirar sarakuna 3 masu daraja ta 2 ya tsallake karatu a Majalisar Dokokin Kano

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Kudurin kirkirar sarakuna masu daraja ta biyu ya tsallake karatun farko a majalisar dokokin Kano

Sabon kudurin ƙirƙirar sakaruna masu daraja ta biyu ya tsallake karatu na farko a zauren Majalisar Dokokin Jihar Kano.

Sabbin Sarakunan da aka ƙirƙira dai sune na Rano, Ƙaraye da kuma Gaya.

A cewar ƙudurin, dukkansu za su kasance ne ƙarƙashin Sarkin Kano, wanda shi kaɗai ne mai daraja ta ɗaya yanzu a jihar.

Kananan hukumomin da za su kasance ƙarƙashin Sarkin Rano sune Rano Kibiya da Bunkure, shi kuma na Karaye yana da kananan hukumomin Karaye da Rogo.

Matakin na zuwa ne bayan Majalisar ta rushe dokar da ta kirkiri sabbin masarautu guda biyar a jihar ta shekara ta 2019, tare da rushe sarakunan da aka naɗa musu.

Daga bisani dai Gwamnan Jihar, Abba Kabir Yusuf, ya dawo da Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II kan kujerarsa, inda ya sauke Aminu Ado Bayero da sauran sarakunan guda hudu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp