Home DUNIYA Gwamnan Kano ya kadu bisa rasuwar ‘Yan uwan Kwamishina a jihar

Gwamnan Kano ya kadu bisa rasuwar ‘Yan uwan Kwamishina a jihar

Gwamnan jihar Kano Abba kabir Yusuf ya bayyana kaduwar sa bisa mutuwar ‘yan uwa da ‘yar kwamishinan ma’aikatar ilimi mai zurfi na jihar Dr. Yusuf Ibrahim Kofar Mata. sakamakon iftila’in gobara.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da darakta yada labaran Gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa PRNigeria, wadda ta ambaci gwamnan na nuna damuwa gami da kaduwa bias iftila’in gobarar da ya fada kan ‘yan uwan kamishinan mata guda biyu da kuma ‘yar sa.

Gwamnan Abba ya bayyana gobarar matsayin tashin hankali, wanda ya haddasa masa kaduwa duba da yadda ta kai ga rasa rayukan mutane 3 cikin al’ummar jihar kano, gami da rasa dukiya mai tarin yawa.

Sanarwa ta ce a madadin gwamantin jihar Kano, majalisar zartaswa, da al’ummar jihar Kano suna mika sakon ta’aziyya ga kwamishinan da ‘yan uwa da iyalai, tare da fatan Allah ya karbi shahadar su, ya kuma kiyaye aukuwar hakan anan gaba.

A ranar laraba ne dai Dr. kofara mata ya wallafa wani labara a shafin sa na Facebook, dake cewa gobara ta hallaka masa ‘yan uwan sa mata biyu tare da ‘yar sa guda daya.

A cewar sanarwar, ‘yarsa Maimuna (Islam) da babbar yayarsa Hajiya Khadija da matar dan uwansa Hajiya Juwairiyya sun rasu sakamakon gobarar da ta tashi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp