Home DUNIYA Gwamnan Kano ya kadu bisa rasuwar ‘Yan uwan Kwamishina a jihar

Gwamnan Kano ya kadu bisa rasuwar ‘Yan uwan Kwamishina a jihar

Gwamnan jihar Kano Abba kabir Yusuf ya bayyana kaduwar sa bisa mutuwar ‘yan uwa da ‘yar kwamishinan ma’aikatar ilimi mai zurfi na jihar Dr. Yusuf Ibrahim Kofar Mata. sakamakon iftila’in gobara.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da darakta yada labaran Gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa PRNigeria, wadda ta ambaci gwamnan na nuna damuwa gami da kaduwa bias iftila’in gobarar da ya fada kan ‘yan uwan kamishinan mata guda biyu da kuma ‘yar sa.

Gwamnan Abba ya bayyana gobarar matsayin tashin hankali, wanda ya haddasa masa kaduwa duba da yadda ta kai ga rasa rayukan mutane 3 cikin al’ummar jihar kano, gami da rasa dukiya mai tarin yawa.

Sanarwa ta ce a madadin gwamantin jihar Kano, majalisar zartaswa, da al’ummar jihar Kano suna mika sakon ta’aziyya ga kwamishinan da ‘yan uwa da iyalai, tare da fatan Allah ya karbi shahadar su, ya kuma kiyaye aukuwar hakan anan gaba.

A ranar laraba ne dai Dr. kofara mata ya wallafa wani labara a shafin sa na Facebook, dake cewa gobara ta hallaka masa ‘yan uwan sa mata biyu tare da ‘yar sa guda daya.

A cewar sanarwar, ‘yarsa Maimuna (Islam) da babbar yayarsa Hajiya Khadija da matar dan uwansa Hajiya Juwairiyya sun rasu sakamakon gobarar da ta tashi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp