Home General Gwamnatin jihar Katsina na shirin samar da Dokar “Iddah” ga matan Jihar

Gwamnatin jihar Katsina na shirin samar da Dokar “Iddah” ga matan Jihar

Gwamnatin jihar Katsina dake arewa maso yammacin Nijeriya na kokarin samar da wata sabuwar dokar kan iddar mata Mai suna “Iddah Period Law”, domin baiwa mata ma’aikatan gwamnati damar zama a gida na tsawon wata hudu da kwana goma idan mazajensu suka rasu.

Shugaban ma’aikatan jihar Katsina, Alhaji Falalu Bawale ne ya bayyana haka yayin da yake ganawa da manema labarai.

A cewarsa, gabatar da sabuwar dokar ya biyo bayan kudurin da majalisar dokokin jihar ta gabatar, inda ta bukaci gwamnatin jihar ta duba batun wa’adin Iddah wanda hukumar zartaswa ta amince da shi , tare da yin aiki da shawarwarin da majalisar zartaswa ta gabatar.

Ya kara da cewa, tuni aka fitar da wata takarda ga dukkan ma’aikatun Jihar da na Kananan hukumomin domin baiwa mata ma,aikata damar gudanar da iddah a lokacin da bukatar hakan ta taso.

wannan dai na zuwa ne dai dai da Lokacin da Dan Majalisar tarayya na jamiyyar APC daga jihar Niger ya gabatar da wani kudiri makamancin haka na neman ba wa matan da mazansu suka rasu damar tafiya hutu tare da cikakken albashin ma’auratan da suka rasu, inda kudurin ya tsallake karatu na biyu a zauren majalisar.

Iddah ga matan da mazajen su suka mutu na guda cikin sharuddan da addinin muslunci yayiwa mata a yayin gudanar da ruyuwarsu ta yau da kulum muddin dai bukatar hakan ta taso.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp