Home General Kungiyar Matasan Arewa ta Janye zanga-zangar data shirya a yankin

Kungiyar Matasan Arewa ta Janye zanga-zangar data shirya a yankin

Ƙungiyar Shugabannin Matasan Arewacin Najeriya ta janye zanga-zangar da ta shirya gudanarwa a faɗin ƙasar.
Shugaban Ƙungiyar shuwagabannin Matasan Najeriya Kwamared Murtala Mohammed Gamji ne ya sanar da hakan, ta cikin wani taron manema labarai da suka gudanar yau a Abuja, inda ya ce sun janye ƙudirin nasu ne a sakamakon yadda suka yi zargin sheɗanci ya shigo cikin shirin nasu.
Jaridar GTR ta ruwaito Gamji na cewa sun ɗauki matakin ne biyo bayan yadda suka gano wasu ɓata gari suna shirya wani mummunan abu, ta hanyar fakewa da zanga-zangar domin rikita ƙasar gaba-ɗaya.
A cewar Gamji ” Ni na fara shirya zanga-zangar kuma wasu mutane sun gayyace ni mun zauna dasu, harma suka shaida min so suke ayi zanga-zangar a iya Jihar Kaduna da Jos da kuma Babban birnin tarayya Abuja, saboda haka dole mu janye shirin namu tunda wasu sun fara yunƙurin cimma burinsu ta hanyar yin amfani damu”.
domin haka ya ce suna kira da dukkan wani ɓangare na al’ummar dake yankin arewa da suyi watsi dayin zanga-zangar, su dawo a haɗa kai abi hanyoyin da suka dace domin neman haƙƙin talakawan ƙasar a wurin shugabanni.
Bugu da ƙari ya kuma shawarci Jami’an tsaro da suyi gaggawar kama dukkan waɗanda suka fito zanga-zangar, domin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a dukkan sassan Najeriya.
A ƙarshe ya jaddada cewa suna barranta kansu da yadda ake zagin Malamai, dama yunƙurin fakewa da zanga-zangar wajen lalata dukiyar mutane koma ƙona kayan Gwamnati wanda babu abinda zai haifar illa ƙarin wasu matsaloli a faɗin ƙasar.
PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp