Tsohon Ministan wasanni da ci gaban matasa a gwamnatin Buhari, Sunday Dare ya shawarci matasan kasar nan a kan hanyar samun saukin halin da ake ciki.
Tsohon Ministan ya ce akwai wata hanya da za a bi a maimakon a tafi zanga-zangar gama gari da aka shirya za a yi na kwanaki 15.
A wata hira da tsohon Ministan ya yi ta shafinsa na X, ya ce har yanzu jama’a na kokarin farfado wa daga cikin halin da zanga-zangar endSARS ta jefa ‘yan Najeriya ba.
Read Also:
Tsohon Minista a gwamnatin Buhari, Sunday Dare ya gargadi matasa kan illar da zai iya biyo bayan zanga-zangar gama garin da suke shirin farawa.
ya ce akwai fargabar bata-gari za su iya shiga rigar masu zanga-zanga wajen tayar da hatsaniya a kasar nan.
Dare ya bayyana cewa kamata ya yi matasan kasar nan su zauna da gwamnati domin neman mafita.
Ya ce kamata ya yi a zauna, a tattauna da gwamnati a kan hanyar da ta fi dace wa wajen magance koken ‘yan kasa.
PRNigeria Hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1190 days 13 hours 28 minutes 7 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1172 days 15 hours 9 minutes 32 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com