Sakataren Gwamnatin tarayya, George Akume ya shiga ganawa da ministoci a yayin da ake shirin fara zanga-zanga kan tsadar rayuwa a fadin Najeriya.
Ganawar wacce ke gudana cikin sirri ta samu halartar ministoci sama da 40 na gwamnatin shugaba Tinubu.
Wasu daga cikin ministocin da aka hango a wajen ganawar sun hada da: Nyesom Wike na birnin tarayya Abuja da ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar da Zephnia Jisalo da Tahir Mamman da Atiku Bagudu.
Read Also:
Sauran ministocin sun hada da Wale Edun na kudi da ministan yada labarai Mohammed Idris da sauransu.
wannan dai na zuwa ne bayan, shugaban kasa Tinubu ya roki matasan Najeriya da su dakata daga shiga zanga zangar ta ‘EndBadGovernance’ da aka tsara farawa a wata mai kamawa.
ko da yake wasu wata kungiya da tayi ikirarin shirya zanga zangar tun da fari a Arewacin kasar ta janye yayin da wata kungiya kuma a jihar kano tace zanga – zanga babu fashi
PRNigeria Hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1190 days 11 hours 43 minutes 19 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 24 minutes 44 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com