Ya kamata gwamnatin Najeriya ta kare masu saka jari na cikin gida – MAN

Ƙungiyar masu masana’antu ta Najeriya ta yi gagaɗi ga gwamnatin ƙasar kan ƙoƙarin gurgunta masana’antun cikin gida.

Ƙungiyar ta yi kiran yin taka-tsantsan da masu ruwa da tsaki kan harakar man fetur da kuma hukumomi sakamakon rikicin gwamnatin tarayya da Matatar Dangote.

Babban Daraktan ƙungiyar Ajayi Kabir ya ce hukumomin gwamnati da ke aikin sa-ido yakamata su inganta yanayi mai kyau na kasuwanci da zuba jari comin ci gaban masana’antun cikin gida.

Ya ce babu wata hukuma da ta kamata ta kawo tarnaki ga babbar masana’anta ta cikin gida kamar Matatar Dangote.

Ya ƙara da cewa masu zuba jari na cikin gida a Najeriya kamar Matatar Dangote suna taka rawa sosai wajen bunƙasa tattalin arziki da biyan haraji da samar da ayyukan yi da kuma ci gaba. Don haka a cewarsa ya kamata a ba su goyon bayan da suke buƙata domin ci gaban kasuwancinsu.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1187 days 23 hours 36 minutes 3 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1170 days 1 hour 17 minutes 28 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com