Home General Ya kamata gwamnatin Najeriya ta kare masu saka jari na cikin gida...

Ya kamata gwamnatin Najeriya ta kare masu saka jari na cikin gida – MAN

Ƙungiyar masu masana’antu ta Najeriya ta yi gagaɗi ga gwamnatin ƙasar kan ƙoƙarin gurgunta masana’antun cikin gida.

Ƙungiyar ta yi kiran yin taka-tsantsan da masu ruwa da tsaki kan harakar man fetur da kuma hukumomi sakamakon rikicin gwamnatin tarayya da Matatar Dangote.

Babban Daraktan ƙungiyar Ajayi Kabir ya ce hukumomin gwamnati da ke aikin sa-ido yakamata su inganta yanayi mai kyau na kasuwanci da zuba jari comin ci gaban masana’antun cikin gida.

Ya ce babu wata hukuma da ta kamata ta kawo tarnaki ga babbar masana’anta ta cikin gida kamar Matatar Dangote.

Ya ƙara da cewa masu zuba jari na cikin gida a Najeriya kamar Matatar Dangote suna taka rawa sosai wajen bunƙasa tattalin arziki da biyan haraji da samar da ayyukan yi da kuma ci gaba. Don haka a cewarsa ya kamata a ba su goyon bayan da suke buƙata domin ci gaban kasuwancinsu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp