Home General NLC ta musanta Janyewar shiga Zanga Zanga a Nijeriya

NLC ta musanta Janyewar shiga Zanga Zanga a Nijeriya

Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC), ta ce bata janye daga shiga zanga-zangar matsin rayuwar da ake shirin gudanarwa a ƙasar ba.

Ƙungiyar ta sanar da hakan ne ta cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, inda ta barranta kanta da labarin da ake yaɗawa na cewa ta fasa shiga zanga-zangar.
Sanarwar da Shugaban Ƙungiyar na ƙasa Kwamared Joe Ajaero ya sanyawa hannu ta ƙara da cewa, duk da ba ƙungiyar ce ta shirya zanga-zangar ba amma hakan bazai hana ta shiga ba, saboda halin ƙunci da matsin da talakawan ƙasar suke ciki a sakamakon wasu matakan da gwamnatin ƙasar ta ɗauka.
Adan haka ne ƙungiyar za ta shiga zanga-zangar domin taya al’ummar ƙasar wannan yaƙi, na nema wa kansu sauƙi a cikin mummunan halin da suke ciki.
Haka kuma ta buƙaci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya zauna da masu shirya zanga-zangar a teburin sulhu, dangane da buƙatun da suke dashi ta yadda za’a magance matsalar ba tare amfani da ƙarfin mulki ba.
A ƙarshe ƙungiyar tayi fatan Gwamnatin tarayya dana jihohi zasu waiwayi koken ‘yan ƙasar, kuma su biya musu dukkan buƙatun su domin gudun faɗawar ƙasar cikin yanayi da ba’a tsammani.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp