”Arewa Media Writers” ta umarci mambobinta su fito Zanga Zanga

Ƙungiyar Marubutan Arewa a Kafofin sadarwa na zamani wato Arewa Media Writers, ta umarci dukkan Mambobinta na Jihohi 19 har da Abuja su fito Zanga-zangar lumana a ranar Alhamis 1 ga watan Augusta.

Ƙungiyar ta sanar da hakan ne ta cikin wata sanarwa da Mataimakin Daraktan yaɗa labaranta na ƙasa Muhammad Kwairi Waziri ya aiko wa manema labarai a safiyar yau Litinin. inda ta ce ya zama wajibi su fito domin ƙara sanar da gwamnati matsalolin da ake fuskanta a yankin Arewa.

Sanarwar ƙungiyar ta ƙara da cewa al’ummar Arewa suna cikin matslolin rashin tsaro, yunwa, tsadar rayuwa, amma kuma gwamnati ta kasa magance musu matsalolin.

Haka zalika ƙungiyar ta ƙara jaddada wa magoya bayanta cewa babu fitowa da makami ko cin zarafin wani, ko ɗaukar kayan wani a yayin zanga-zangar, wanda dama ba fito na fito za’ai da gwamnati ba, illa kira ga hukuma da su san halin matsi da ƙuncin da al’umma suke ciki.

A ƙarshe ta yi kira ga dukkan masu fitowa zanga-zangar da su bawa jami’an tsaro haɗin kai yayin fitar, kuma su kula da bin doka da oda ta ƙasa Nijeriya.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 33 minutes 56 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 15 minutes 21 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com