Home General ”Arewa Media Writers” ta umarci mambobinta su fito Zanga Zanga

”Arewa Media Writers” ta umarci mambobinta su fito Zanga Zanga

Ƙungiyar Marubutan Arewa a Kafofin sadarwa na zamani wato Arewa Media Writers, ta umarci dukkan Mambobinta na Jihohi 19 har da Abuja su fito Zanga-zangar lumana a ranar Alhamis 1 ga watan Augusta.

Ƙungiyar ta sanar da hakan ne ta cikin wata sanarwa da Mataimakin Daraktan yaɗa labaranta na ƙasa Muhammad Kwairi Waziri ya aiko wa manema labarai a safiyar yau Litinin. inda ta ce ya zama wajibi su fito domin ƙara sanar da gwamnati matsalolin da ake fuskanta a yankin Arewa.

Sanarwar ƙungiyar ta ƙara da cewa al’ummar Arewa suna cikin matslolin rashin tsaro, yunwa, tsadar rayuwa, amma kuma gwamnati ta kasa magance musu matsalolin.

Haka zalika ƙungiyar ta ƙara jaddada wa magoya bayanta cewa babu fitowa da makami ko cin zarafin wani, ko ɗaukar kayan wani a yayin zanga-zangar, wanda dama ba fito na fito za’ai da gwamnati ba, illa kira ga hukuma da su san halin matsi da ƙuncin da al’umma suke ciki.

A ƙarshe ta yi kira ga dukkan masu fitowa zanga-zangar da su bawa jami’an tsaro haɗin kai yayin fitar, kuma su kula da bin doka da oda ta ƙasa Nijeriya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp