Gwamnatin Kano ta magantu kan halin da ake ciki a jihar

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ce ba za su saurarawa duk masu kokarin tayar da fitina da sunan zanga-zanga a fadin jihar kano ba.

Gwamnan ya furta haka ne yau a gidan Gwamnati Lokacin da yake karbar takardar korafi daga wasu jagororin al’umma kan dalilin da ya sa Suka fara gudanar da zanga Zanga a yau Alhamis.

Gwamnan ya kara da cewa duk da yake kudin tsarin mulkin kasa ya bayar da dama gudanar dazanga-zanga lumana ,amma gwamnati ba za ta zuba Ido wasu bata gari suyi amfani da ita ba wajen sace-sace kone-kone da fasa shagunan alumma, in da ya ce jami,an tsaro za su yi aiki ba sani ba sabo ga duk Wanda aka kama da hannu a ciki.

Gwamnan ya yabawa jami’an tsaro bisa yadda Suka jajirce wajen kakkabe batagari da ke Neman tayar da fitina a jihar kano.

Ya Kuma yabawa kungiyar da ta kawo takardar kokenta da cewa zai Jagorancin wasu daga cikin al’ummar kano har zuwa fadar Shugaban kasa don Mika sakonsu kan irin halin matsin da alumma ke ciki.

daga bisani  Gwamnan ya ja hankalin ‘ya siyasa da su guji yin amfani da bata gari don cimma bukatunsu

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 54 minutes 18 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 35 minutes 43 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com