Home Labarai Gwamnatin Kano ta magantu kan halin da ake ciki a jihar

Gwamnatin Kano ta magantu kan halin da ake ciki a jihar

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ce ba za su saurarawa duk masu kokarin tayar da fitina da sunan zanga-zanga a fadin jihar kano ba.

Gwamnan ya furta haka ne yau a gidan Gwamnati Lokacin da yake karbar takardar korafi daga wasu jagororin al’umma kan dalilin da ya sa Suka fara gudanar da zanga Zanga a yau Alhamis.

Gwamnan ya kara da cewa duk da yake kudin tsarin mulkin kasa ya bayar da dama gudanar dazanga-zanga lumana ,amma gwamnati ba za ta zuba Ido wasu bata gari suyi amfani da ita ba wajen sace-sace kone-kone da fasa shagunan alumma, in da ya ce jami,an tsaro za su yi aiki ba sani ba sabo ga duk Wanda aka kama da hannu a ciki.

Gwamnan ya yabawa jami’an tsaro bisa yadda Suka jajirce wajen kakkabe batagari da ke Neman tayar da fitina a jihar kano.

Ya Kuma yabawa kungiyar da ta kawo takardar kokenta da cewa zai Jagorancin wasu daga cikin al’ummar kano har zuwa fadar Shugaban kasa don Mika sakonsu kan irin halin matsin da alumma ke ciki.

daga bisani  Gwamnan ya ja hankalin ‘ya siyasa da su guji yin amfani da bata gari don cimma bukatunsu

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp