Home Labarai Gwamnatin Kano ta magantu kan halin da ake ciki a jihar

Gwamnatin Kano ta magantu kan halin da ake ciki a jihar

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ce ba za su saurarawa duk masu kokarin tayar da fitina da sunan zanga-zanga a fadin jihar kano ba.

Gwamnan ya furta haka ne yau a gidan Gwamnati Lokacin da yake karbar takardar korafi daga wasu jagororin al’umma kan dalilin da ya sa Suka fara gudanar da zanga Zanga a yau Alhamis.

Gwamnan ya kara da cewa duk da yake kudin tsarin mulkin kasa ya bayar da dama gudanar dazanga-zanga lumana ,amma gwamnati ba za ta zuba Ido wasu bata gari suyi amfani da ita ba wajen sace-sace kone-kone da fasa shagunan alumma, in da ya ce jami,an tsaro za su yi aiki ba sani ba sabo ga duk Wanda aka kama da hannu a ciki.

Gwamnan ya yabawa jami’an tsaro bisa yadda Suka jajirce wajen kakkabe batagari da ke Neman tayar da fitina a jihar kano.

Ya Kuma yabawa kungiyar da ta kawo takardar kokenta da cewa zai Jagorancin wasu daga cikin al’ummar kano har zuwa fadar Shugaban kasa don Mika sakonsu kan irin halin matsin da alumma ke ciki.

daga bisani  Gwamnan ya ja hankalin ‘ya siyasa da su guji yin amfani da bata gari don cimma bukatunsu

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp