Gwamnatin jihar kano ta saka dokar hana fita ta tsawon sa’oin 24, bayan bata – gari sun shiga cikin masu gudanar da zanga zangar lumana a jihar.
Gwamnan jihar Abba Kabir yusuf ne ya bayyana hakan yayin da yake ganaw da anema labarai a fadar gwamnatin jihar a yammacin Alhamis dake matsayin ranar farko ta fara zanga zangar.
Read Also:
Ya ce an saka dokar ne domin a dakile sace-sace da fashe-fashen kayan gwamnati da na al’umma da wasu ɓatagari ke yi a ƙarƙashin zanga-zangar.
Ya ce wasu ‘Yan siyasa ne da ba sa son ci gaban Kano ke daukar nauyin yan daba wadanda su ka fake da zanga-zanga su ka fara kai hare-hare.
Ya kuma umarci jami’an tsaro da su gaggauta fara aiwatar da dokar nan take.
PRNigeria Hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1188 days 19 hours 47 minutes 31 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1170 days 21 hours 28 minutes 56 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com