Home Labarai ‘Yan Sanda sun tarwatsa masu Zanga-Zanga a Birnin Abuja

‘Yan Sanda sun tarwatsa masu Zanga-Zanga a Birnin Abuja

Jami’an ‘yansanda sun harba hayaƙi mai sa hawaye kan masu zanga-zanga a filin wasa na MKO Abiola da ke birnin Abuja, domin tarwasu.

Masu zanga-zangar – waɗanda adadinsu bai kai yadda suka fito a ‘yan kwanakin bayan nan ba – sun taru a filin wasan domin ci gaba da gudanar da zanga-zangar.

Wasu matasan ƙasar ne dai suka shirya zanga-zangar da suka ce ta kwana 10 ne da nufin nuna adawa da matsin rayuwa da ake ciki.

To sai dai bayanai sun ce sa’o’i bayan fara zanga-zangar tasu sai ‘yansanda suka fara harba musu tiyagas da nufin tarwatsa su.

Hukumomin birnin Abuja ne dai suka ware filin wasan a matsayin wurin da za a gudanar da zanga-zangar, bayan umarnin wata kotu ta hana masu zanga-zangar zuwa wasu sassan birnin.

Ko a ranar Juma’a ma ‘yansandan sun harba wa masu zanga-zangar hayaƙi mai sa hawaye a shataletalen Berger da ke tsakiyar Abuja.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp