An saka dokar hana fita a jihar Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanya dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 24 a babban birnin jihar da kuma Zariya.

Gwamnatin ta ce ta ɗauki matakin ne “bayan nazarin yanayin tsaro a jihar sakamakon tarzomar da aka samu” biyo bayan zanga-zangar da ake yi a sassan Najeriya saboda kuncin rayuwa.

Wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar ta hannun kwamishina mai lura da harkokin tsaro a jihar, Samuel Aruwan ta ce “akwai ƙwararan hujjoji da ke nuna cewa ɓata gari sun ƙwace zanga-zangar, waɗanda suka koma satar kaya da ɓarnata dukiyar gwamnati.”

Gwamnatin ta shawarci al’ummar jihar da su kiyaye da doka da kuma kasancewa a cikin gida, a yayin da jami’an tsaro kuma za su ci gaba da aiki don tabbatar da tsaron lafiyar al’umma.

Jihar kaduna, ta zamo ta baya-bayannan da aka sanya dokar hana fita saboda yadda zanga-zangar ta rikiɗe zuwa tarzoma.

Kaduna na daga cikin jihohin da aka sanar cewa an samu asarar rayuka tun bayan ɓarkewar zanga-zangar a ranar Alhamis.

An sanya irin wannan dokar a jihohin Kano da Jigawa da Borno da Yobe da Katsina da kuma Filato.

Kodayake, an dage dokar a wasu jihohin, yayin da a wasu kuma aka sassauta dokar.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1187 days 17 hours 51 minutes 20 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1169 days 19 hours 32 minutes 45 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com