Home Labarai An saka dokar hana fita a jihar Kaduna

An saka dokar hana fita a jihar Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanya dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 24 a babban birnin jihar da kuma Zariya.

Gwamnatin ta ce ta ɗauki matakin ne “bayan nazarin yanayin tsaro a jihar sakamakon tarzomar da aka samu” biyo bayan zanga-zangar da ake yi a sassan Najeriya saboda kuncin rayuwa.

Wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar ta hannun kwamishina mai lura da harkokin tsaro a jihar, Samuel Aruwan ta ce “akwai ƙwararan hujjoji da ke nuna cewa ɓata gari sun ƙwace zanga-zangar, waɗanda suka koma satar kaya da ɓarnata dukiyar gwamnati.”

Gwamnatin ta shawarci al’ummar jihar da su kiyaye da doka da kuma kasancewa a cikin gida, a yayin da jami’an tsaro kuma za su ci gaba da aiki don tabbatar da tsaron lafiyar al’umma.

Jihar kaduna, ta zamo ta baya-bayannan da aka sanya dokar hana fita saboda yadda zanga-zangar ta rikiɗe zuwa tarzoma.

Kaduna na daga cikin jihohin da aka sanar cewa an samu asarar rayuka tun bayan ɓarkewar zanga-zangar a ranar Alhamis.

An sanya irin wannan dokar a jihohin Kano da Jigawa da Borno da Yobe da Katsina da kuma Filato.

Kodayake, an dage dokar a wasu jihohin, yayin da a wasu kuma aka sassauta dokar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp