Home Labarai Mun Kama ‘yanƙasar Poland bakwai a Kano kan ɗaga tutar Rasha a...

Mun Kama ‘yanƙasar Poland bakwai a Kano kan ɗaga tutar Rasha a zanga-zanga – DSS

Jami’an tsaro a Najeriya sun kama ‘yan ƙasar Poland bakwai bisa zargin ɗaga tutocin Rasha yayin zanga-zanga kan tsadar rayuwa a jihar Kano da ke arewacin ƙasar.

Kakakin rundunar tsaron farin kaya, Peter Afunanya, ya faɗa yayin taron manema labarai a yau Laraba cewa sun kama su ne lokacin da jami’ansu ke ƙoƙarin tabbatar da tsaro.

Sai dai bai yi ƙarin bayani ba game da ko su wane ne, amma ba farautar ‘yan ƙasar ta Poland a Najeriya suke yi ba.

Kamfanin labarai na Reuters ya ruwaito jakadan Poland a Najeriya, Stanislaw Gulinski, yana tabbatar da kamen yayin ganawar da jakadu suka yi da gwamnatin Najeriya ranar Laraba a Abuja.

“An kama su kwana biyu da suka wuce a Kano, abu na ƙarshe da na ji shi ne ana shirin kawo su Abuja a jirgi,” in ji shi.

Sai dai ya ƙi yin ƙarin bayani lokacin da Reuters ya tuntuɓe shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp