Home Labarai Ina sane da halin kuncin da kuke ciki – Tinubu

Ina sane da halin kuncin da kuke ciki – Tinubu

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake yin roƙo ga ƴan ƙasar su ƙara yi wa gwamnatinsa haƙuri inda ya ce sauƙi na nan tafe.

Shugaban ya sake yin jawabi ne ga ƴan Najeriya a wani bidiyo da ya wallafa a shafinsa na X ranar Laraba bayan jawabin farko da ya yi a ranar Lahadi saboda zanga-zangar tsadar rayuwa da kuma adawa da matakansa na tattalin arziki.

A cikin jawabin shugaban, ya nanata cewa yana sane da ƙuncin rayuwa da ƴan Najeriya suka shiga sakamakon janye tallafin fetur.

Ƴan Najeriya da dama ne suka fantsama a titunan biranen ƙasar domin zanga-zangar tsadar rayuwa, inda wasunsu da dama ke kira ga shugaban ya dawo da tallafin da ya cire na man fetur da suka ce ya jefa su cikin mawuyacin hali na tsadar rayuwa.

Amma a sabon jawabinsa, shugaban ya ce yana sane da wahalar da ƴan Najeriya ke ciki tare da nanata cewa wahala ce ta ɗan ƙaramin lokaci.

“Wannan lokacin zai iya zama mai wahala a gare mu amma ina son mu yi hangen gaba a cikin wahalar da muke ciki da kuma la’akari da babbar manufar. Mun yi tsare-tsare masu kyau kuma na san za su yi aiki,” in ji Shugaba Tinubu.

Sai dai shugaban ya amince cewa tsare-tsaren da gwamnatinsa ke ɗauka sun ƙara wa ƴan Najeriya raɗaɗin janye tallafin fetur.

Amma ya ce ya yi imanin matakan gwamnatinsa ke ɗauka za su magance matsalolin tattalin arzikin da Najeriya ke ciki.

“Ina roƙon ku, ku yi haƙuri tare da imanin cewa za mu iya da kuma damuwar da muke nunawa kan buƙatunku. Za mu fita daga cikin wannan ƙangin, kuma saboda matakan da muke ɗauka Najeriya za ta samu ci gaba da kuma more makomarta,” a cewar shugaba Tinubu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp