Home Labarai Al’ummar Nijeriya na shakku kan fara aikin matatar mai ta Fatakwal

Al’ummar Nijeriya na shakku kan fara aikin matatar mai ta Fatakwal

Kungiyar dilalan man fetur ta kasar nan tace nan da makwanni uku masu zuwa matatar mai ta fatakwal zata fara aiki yadda ya kamata, domin cimma umarnin da gwamnatin tarayya ta bayar na watan Agusta.

Haka kuma kungiyar tace matatar zata ke fitar da mai lita miliyan 10 zuwa miliyan 12 ga ‘yan kasuwa.

Contirolan ayyukan na kungiyar Zarma Mustapha ne ya bayyana hakan yayyin da yake ganawa da kafar yada labarai ta NTA, inda yace matatar man zata habaka samar da man a kasar nana daga lita miliyan 11 zuwa 15 a ko wacce, gami da samar da wadataccen makamashi.

Haka kuma matatar zata yi aiki ne bisa zaman kanta, kuma zata sayar da man ne bisa farashin kasuwa ba tare da gwamnatin tarayya tayi mata katsandan ba.

Ko da yace bayan bayyana wannan kudiri Al’ummar kasar nan sun bayyana cewa sun gaji da gafara sa basu ga kaho ba, duba da yadda aka yi ta yi musu alkawurra amma babu guda daya da aka cika akan matatun na kasar nan.

Idan dai za’a iya tunawa mahukunta a kasar nan sun bayyanawa al’umma cewa matata zata fara aiki watan disambar 2023, idan aka hada da wannan alkawari gwamantin tarayyar kasar nan tayi alkawarin sau hudu kenan tun bayan darewarta kan karagar mulki.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp