Jihar Kano ta sake rabauta da mukami a mulkin Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya amince da nadin Farfesa Abdullahi Saleh Usman a matsayin shugaban hukumar kula da alhazai ta Nigeria (NAHCON).

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar Ajuri Ngelale ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

Farfesa Abdullahi Sale fitaccen malamin Addinin musulunci ne wanda ya yi digirinsa na farko a cibiyoyin ilimi na Musulunci guda biyu – Jami’ar Madina da Jami’ar Peshawar da ke Pakistan.

Ya kuma kware wajen gudanar da aikin Hajji, inda ya taba rike mukamin Shugaban Hukumar Jin dadin Alhazai ta Jihar Kano, kuma ya samu nasarar mai tarin yawa a lokacinsa.

Sabon mukamin nasa zai fara aiki ne bayan Majalisar kasa ta amince da nadin.

Shugaban ƙasar ya yiwa sabon shugaban hukumar ta NAHCON fatan alkhairi tare da fatan zai gudanar da aikinsa bisa gaskiya da rikon amana ga alhazan Nigeria .

Idan dai za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito ana zargin tsohon shugaban hukumar ta NAHCON Jalal Arabi da almundahanar kudade bayan kammala ibadar aikin hajjin bana.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 41 minutes 37 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 23 minutes 2 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com