Home Labarai NLC na tattaunawa kan gayyatar da ‘yan sandan suka yiwa Ajaero

NLC na tattaunawa kan gayyatar da ‘yan sandan suka yiwa Ajaero

Manyan jagororin ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya NLC da suka hada da shugabanta, Joe Ajaero, sun hallara a hedikwatar ƙungiyar ta NLC domin gudanar da wani taron gaggawa na shugabannin ƙungiyar.

Taron ya biyo bayan sammacin da rundunar ‘yan sandan Najeriya ta yi wa Ajaero na ya gurfana a gabanta domin amsa tambayoyi kan zarge-zargen da suka shafi samar da kuɗaɗe ga ayyukan ta’addanci, da cin amanar kasa, da kuma aikata laifuka ta shafukan intanet.

Umarnin ‘yan sanda dai ya buƙaci Ajaero ya gabatar da kansa da misalin karfe 10:00 na safiyar yau Talata domin amsa tambayoyi.

A ranar Litinin ne aka gayyaci Ajaero ta hanyar wata wasiƙa mai dauke da sa hannun ACP Adamu Muazu a madadin mataimakin kwamishinan ƴansanda mai kula da ɓangaren tattara bayanan sirri.

ko dai a makwannin da suka gabata dakarun ‘yan sandan sun kutsa kai ofishin kungiyar dake birnin tarayya Abuja, inda kungiyar ta yi zargin sun yi mata barna a wajen adana litattafan ta gami da tilastawa masu gadi sai sun basu mukullan ofisoshin dake hawa na biyu na ginin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp