Home General Gwamnan Jihar Sokoto ya magantu kan kisan sarkin Gobir

Gwamnan Jihar Sokoto ya magantu kan kisan sarkin Gobir

Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu ya miƙa ta’aziyarsa a kan rasuwar Hakimin Gatawa Alhaji Isa Muhammed Bawa, wanda ya rasu a hannun masu garkuwa da mutane.

A saƙon jajen, gwamnan ya ce yana miƙa saƙon jajensa zuwa ga iyalan marigayin da mutanen Sabon Birni da dukkan mutanen jihar.

Cikin wata sanarwa da Sakataren Watsa Labaransa, Abubakar Bawa ya fitar, Aliyu ya ce gwamnatinsa ba za ta huta ba har sai an kawo ƙarshen ayyukan ƴan bindiga a jihar.

Gwamna Aliyu ya bayyana kisan a matsayin “rashin tausayi da dabbanci”, wanda dole a yi Allah-wadai da shi.

Sanarwar ta bayyana mamacin a matsayin mai gaskiya da amana, da son zaman lafiya wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen aiki ga al’umma.

Dokta Aliyu ya yi kira ga jami’an tsaro a jihar da su ƙara ƙoƙari a kan wanda suke yi domin tabbatar da tsaro a jihar, sannan su yi duk mai yiwuwa wajen tabbatar da cewa an kama waɗanda suka kashe hakimin domin su fuskanci hukunci.

Tuni dai Al’ummar garin Sabon Birni a jihar suka gudanar da sallar janazar Sarkin Gobir na Gatawa, Isa Bawa da safiyar yau Alhamis, bayan kashe shi da ƴan bindiga suka yi.

Labarin kisan sarkin ya ɓulla ne a ranar Laraba, bayan da bayanai suka tabbatar da cewa ƴan bindigar sun halaka shi duk da neman kuɗin fansa da suka yi.

Ɗaruruwan mutane ne suka hallara domin gudanar da sallar a garin Sabon Birni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp