Home General Ambaliya-Mutane sama da dubu 40 sun rasa muhallansu a Nijeriya

Ambaliya-Mutane sama da dubu 40 sun rasa muhallansu a Nijeriya

Aƙalla mutum 49 ne suka mutu a Najeriya sakamakon mamakon ruwan sama da ya haddasa ambaliyar a jihohin arewa maso gabashin ƙasar, a cewar hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa.

Kakakin hukumar Manzo Ezekiel, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa a da ya fitar ranar Litinin cewa jihohin Adamawa da Taraba na yankin ne da kuma Jigawa lamarin ya fi shafa, inda mutum sama da 41,344 suka rasa muhallansu.

A shekarar 2022, Najeriya ta fuskanci ambaliyar mafi muni cikin shekara 10, wadda ta yi ajalin mutum aƙalla 600, sannan ta raba miliyan 1.4 da muhallansu tare da lalata jimillar gonaki masu faɗin hekta 440,000.

“Yanzu ne muke shiga ƙololuwar damina, musamman a arewaci kuma lamarin ya tsananta,” a cewar sanarwar.

Zuwa yanzu ruwan ya lalata gonalki masu faɗin hekta 693 yayin da Najeriya ke fama da hauhawar farashin kayayyaki musamman na abinci.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp