Home General Ambaliya-Mutane sama da dubu 40 sun rasa muhallansu a Nijeriya

Ambaliya-Mutane sama da dubu 40 sun rasa muhallansu a Nijeriya

Aƙalla mutum 49 ne suka mutu a Najeriya sakamakon mamakon ruwan sama da ya haddasa ambaliyar a jihohin arewa maso gabashin ƙasar, a cewar hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa.

Kakakin hukumar Manzo Ezekiel, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa a da ya fitar ranar Litinin cewa jihohin Adamawa da Taraba na yankin ne da kuma Jigawa lamarin ya fi shafa, inda mutum sama da 41,344 suka rasa muhallansu.

A shekarar 2022, Najeriya ta fuskanci ambaliyar mafi muni cikin shekara 10, wadda ta yi ajalin mutum aƙalla 600, sannan ta raba miliyan 1.4 da muhallansu tare da lalata jimillar gonaki masu faɗin hekta 440,000.

“Yanzu ne muke shiga ƙololuwar damina, musamman a arewaci kuma lamarin ya tsananta,” a cewar sanarwar.

Zuwa yanzu ruwan ya lalata gonalki masu faɗin hekta 693 yayin da Najeriya ke fama da hauhawar farashin kayayyaki musamman na abinci.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp