Jama’ar garin Matusgi sun kashe ’yan fashin daji 37 a Zamfara

Al’ummar ƙauyen Matusgi da ke Jihar Zamfara sun kashe ’yan fashin daji 37 biyo bayan wani dauki ba dadi da aka yi a kauyen.

Mazauna ƙauyen Matusgi da ke Ƙaramar Hukumar Ƙaura Namoda yunkuro ne a lokacin da ’yan ta’addan suka kai musu hari a ranar Laraba.

Wani wanda abun ya faru a gabansa ya ce  wannan  ab shi ne karon farko da ’yan bindiga suka kwashi kashinnsu a hannun ƙauyen ba.

Ya ce a baya al’ummar ƙauyen sun sha yin fito-na-fito na ’yan fashin daji.

Wata majiya ta shaida wa Aminiya cewa  ’yan fashin daji sun fara harbul kan mai uwa da wabi daga shigar su kauyen.

Suna cikin harbe-harben ne jama’ar garin suka yi musu kawanya, suka nemi hana su tserewa, suna yi musu luguden wuta, har suka kashe ’yan fashin daji da dama.

Hakimin Matusgi, Alhaji Ciroma Muhammad, ya ce bayan ɗauki-ba-daɗin, mutanen ƙauyukan da ke kusa da su sun ce sun ga ’yan fashin daji suna wucewa da gawarwakin ’yan uwansu a kan babura.

“A wancan har suka fice ne ba yi ba, sai sai bayan da suka tafi suka yi kafin muka san sun shigo mana.”

Ya ce sun buƙaci kuɗin fansa N150,000 a kan kowane mutum guda, amma bayan an biya kuɗin mata bakwai kawai suka sako, har yanzu suna riƙe da sauran

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 18 minutes 11 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 59 minutes 36 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com