Home General Jama’ar garin Matusgi sun kashe ’yan fashin daji 37 a Zamfara

Jama’ar garin Matusgi sun kashe ’yan fashin daji 37 a Zamfara

Al’ummar ƙauyen Matusgi da ke Jihar Zamfara sun kashe ’yan fashin daji 37 biyo bayan wani dauki ba dadi da aka yi a kauyen.

Mazauna ƙauyen Matusgi da ke Ƙaramar Hukumar Ƙaura Namoda yunkuro ne a lokacin da ’yan ta’addan suka kai musu hari a ranar Laraba.

Wani wanda abun ya faru a gabansa ya ce  wannan  ab shi ne karon farko da ’yan bindiga suka kwashi kashinnsu a hannun ƙauyen ba.

Ya ce a baya al’ummar ƙauyen sun sha yin fito-na-fito na ’yan fashin daji.

Wata majiya ta shaida wa Aminiya cewa  ’yan fashin daji sun fara harbul kan mai uwa da wabi daga shigar su kauyen.

Suna cikin harbe-harben ne jama’ar garin suka yi musu kawanya, suka nemi hana su tserewa, suna yi musu luguden wuta, har suka kashe ’yan fashin daji da dama.

Hakimin Matusgi, Alhaji Ciroma Muhammad, ya ce bayan ɗauki-ba-daɗin, mutanen ƙauyukan da ke kusa da su sun ce sun ga ’yan fashin daji suna wucewa da gawarwakin ’yan uwansu a kan babura.

“A wancan har suka fice ne ba yi ba, sai sai bayan da suka tafi suka yi kafin muka san sun shigo mana.”

Ya ce sun buƙaci kuɗin fansa N150,000 a kan kowane mutum guda, amma bayan an biya kuɗin mata bakwai kawai suka sako, har yanzu suna riƙe da sauran

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp