Home General Gwamnatin Najeriya ta yi barazanar riƙe albashin likitocin da ke yajin aiki

Gwamnatin Najeriya ta yi barazanar riƙe albashin likitocin da ke yajin aiki

Ma’aikatar lafiyar Najeriya ta bayyana rashin jin daɗinta kan matakin da ƙungiyar likitoci masu neman ƙwarewa ta Najeriya, NARD ta ɗauka na fara yajin aikin gargaɗi na kwana bakwai, duk da ƙoƙarin da gwamnatin ke yi na magance matsalolinsu.

A wata sanarwa da kakakin ma’aikatar, Ado Bako, ya fitar, ya ce gwamnatin ta sanar da aiwatar da dokar “ba aiki, babu albashi” na tsawon kwanakin yajin aikin, ma’ana gwamnati za ta riƙe albashin likitocin da ke yajin aiki har tsawon kwanakin da suka ɗauka suna yajin aikin, kamar yadda dokar ƙwadago ta tanada.

Bako ya jaddada cewa wannan matakin ba yana nufin yin watsi da halascin damuwar likitocin ba ne amma matakin na da nufin tabbatar da cewa muhimman ayyukan kiwon lafiya sun ci gaba da kasancewa ba tare da samun wata katsewa ba don amfanin jama’a.

Likitocin sun fara yajin aikin ne a ranar Litinin, domin matsa wa gwamnati lamba ta ceto abokiyar aikinsu, Dr Ganiyat Popoola da ke hannun masu garkuwa da mutane tun cikin watan Disambar shekarar da ta gabata.

Bako ya ƙara da cewa, ma’aikatar tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro, sun dukufa wajen ganin an sako Dakta Popoola, kuma a halin da ake ciki, akwai tattaunawa mai ƙarfi da ake yi don ganin a kuɓutar da ita daga hannun masu garkuwa da mutanen.

Ma’aikatar ta buƙaci likitocin da su koma kan teburin tattaunawa, inda ta jaddada muhimmancin samar da haɗin kai da kuma dawwamammen mafita kan ƙalubalen da ke fuskantar fannin kiwon lafiya a Najeriya.

Sanarwar ta sake jaddada aniyar ma’aikatar na yin tattaunawa mai ma’ana tare da yin aiki tare da dukkan masu ruwa da tsaki domin cimma maslaha mai dorewa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp