Home General Gwamnatin Kano ta fara daga darajar kananan Asibitocin jihar

Gwamnatin Kano ta fara daga darajar kananan Asibitocin jihar

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bada Umarnin daga darajar karamin asibitin da ke karamar hukumar Albasu zuwa babban Asibiti domin ci gaba da Inganta harkokin kiwon lafiya a karkara

Gwamnan ya bayyana hakan ne Lokacin da ya Kai ziyara duba aikin hanyar kilomita biyar-biyar a yankin.

Hakaza Gwamnan ya bawa ma,aikar ayyuka da gidaje ta Jihar umarnin magance matsalar zai-zayar kasa da ke damun kauyen Hamdullahi na karamar hukumar.

Har ila yau Gwamnan ya bada Umarni fara gyara hanyar da ta tashi daga kwanar Albasu zuwa cikin gari.

daga bisani Gwamnan ya Kai ziyarar gani da ido makarantar kwana ta yammata da ke garin Albasu a wani mataki na fara shirye shiryen sake bude ta domin ci gaba da karatu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp