Home General CISLAC ta zargi CBN da facaka da kudin Nijeriya

CISLAC ta zargi CBN da facaka da kudin Nijeriya

Ƙungiyar CISLAC mai sanya idanu kan ayyukan majalisa a Najeriya ta yi tur da matakin Babban Bankin ƙasar, CBN na zargin facaka da kuɗaɗe masu yawa kan shugabaninsa, lokacin da ake fama da matsalar yunwa da hauhawar farashin kayayyaki.

Ta cikin wata sanarwa da ta fitar mai ɗauke da sa hannun babban daraktanta Auwal Musa Rafsanjani, ƙungiyar ta ce an kashe kuɗaɗen ne kan shugaban bankin Yemi Cardoso da wasu mataimakansa huɗu.

CISLAC ta yi iƙirarin cewa Cardoso da mataimakansa da Majalisar Dattijai ta amince da naɗinsu a watan Satumbar 2023, sun kashe wa kansu naira biliyan 10 wajen sayan motoci masu sulke.

Daga bayanan da CISLAC ta samu ta ce “Mista Cardoso ya bayyana cewa ya saya wa kansa da mataimakansa motoci ƙirar Lexus LX 600 2023. Mataimakan nasa sun haɗa da Emem Usoro da Philip Ikeazor da Bala Bello da kuma Sani Abdullahi.

Majiyar CISLAC daga CBN ta shaida cewa Cardoso ya saya wa kansa wasu motoci biyu ƙirar SUV da zai riƙa amfani da su a Legas da Abuja duk da cewa akwai motoci masu sulke a tawagarsa da yake tafiya da su kusan koda yaushe.

Ƙungiyar ta kuma yi zargin Mista Cardoso ya sayi motoci ƙirar Toyota Camry sabbi guda 20 kan kuɗi naira miliyan 85 kowacce ɗaya, ya kuma raba su ga mambobin kwamitin amintattu na CBN.

Wani rahoton da CISLAC ta samu daga cikin CBN ya ce gwamnan bankin da mataimakansa sun ƙara wa kansu kudin alawus na gida zuwa kusan naira biliyan ɗaya a shekara ɗaya, duk da cewa suna zaune ne a gidajen gwamnati na alfarma da ke Maitama a Abuja.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp