Home General Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Yobe ta tabbatar da harin ‘yan bindiga a...

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Yobe ta tabbatar da harin ‘yan bindiga a Jihar

Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne sun kai hari ƙauyen Mafa a ƙaramar Hukumar Tarmuwa da ke jihar Yobe a arewacin Najeriya, inda suka kashe mutanen da har yanzu ba a san yawansu ba.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya rawaito cewa, maharan sun yi sace-sace da yawa tare da banka wa shaguna da gidaje wuta a ƙauyen.

rundunar ‘yan sandan jihar ta bakin Kakakinta Dungus Abdulkarim ta tabbatar da faruwar lamarin a yau Litinin.

“Har yanzu muna aiki ne domin tabbatar da adadin mutanen da suka rasu dalilin wannan hari, wanda aka kai a ranar Lahadi da misalin ƙarfe 4 na yamma.

“Wasu mutane da ake kira Babagana Goni da Bako Ibrahim ne suka shigar da ƙorafi kan harin a ofishin ‘yan sanda da ke Tarmuwa, kuma dukansu mazauna yankin Mafa ne.

“Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne ɗauke da makamai sun kai hari yankin Mafa a kan babura su sama da 50 kuma sun cinna wa shaguna da gidaje da yawa wuta.

Maharan sun kashe mutane da dama, amma har yanzu ba mu ƙididdige adadin waɗanda harin ya shafa ba,” in ji kakakin ‘yan sandan.

Ya ce bayan sun gama kai harin sun bar wasu makamai da rubutun larabci a jikinsu.

A ranar Juma’a NAN ya rawaito cewa, wasu ‘yan bindiga sun kai hari wata makaranta da ke kusa da garin Geidam tare da kashe ɗalibai uku da jikkata ɗaya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp