Home General Gwamnatin Jigawa tace Adadin Karɓar Rigakafi Ya Ƙaru Zuwa Kashi 49%

Gwamnatin Jigawa tace Adadin Karɓar Rigakafi Ya Ƙaru Zuwa Kashi 49%

Daraktan Kiwon Lafiya a Matakin Farko na Jihar Jigawa, Dr. Shehu Sambo, ya ce adadin rigakafi ya karu daga kashi bakwai cikin dari a shekarar 2016 zuwa kashi 49 cikin dari a shekarar 2021.

Sambo ya bayyana hakan ne yau Laraba a Dutse, yayin taron tattaunawa da manema labarai da kaddamar da gangamin kwanaki biyu kan “Karfi da Inganta Tsarin PHC: Yarjejeniyar UNICEF kan PHC a Jihar Jigawa,” wanda UNICEF da Hukumar Kula da Hakkokin Yara da kuma Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Tarayya suka shirya.

Ya ce an sanya hannu kan yarjejeniyar a shekarar 2022 tsakanin Gwamnatin Jihar Jigawa, Gwamnatin Tarayya, Kungiyar Gwamnonin Najeriya, GAVI, da UNICEF don inganta rigakafi a kai a kai, inganta tsarin PHC, da rage yawan mace-macen mata da yara.

Sambo ya bayyana cewa daya daga cikin dabarun da aka dauka don karfafa yin rigakafi shine karfafa kwamitin kula da aiyukan PHC ta hanyar kyakkyawan shugabanci da jagoranci.

Haka kuma ya bayyana cewa kudaden da aka samu daga GAVI sun basu damar samun karin kudade don daukar ma’aikatan ungozoma da horar da ma’aikatan lafiya a matakin farko don samar da aiyukan da ake bukata ga dukkan wuraren da ke da wahalar isa a fadin jihar.

Ya ce, “Kafin wannan yarjejeniyar, muna da kimanin ungozoma 120 a ɓangaren PHC, amma yanzu, mun dauki fiye da ungozoma 300 don kara ma’aikatan da muke da su. Yanzu haka, muna da fiye da ungozoma 500 da ke aiki a sashen PHC na Jihar Jigawa.”

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp