Jihar Kano na Sahun gaba wajen Mace-Macen mata masu Juna Biyu

Shugaban kungiyar dake rajin kare hakkin Dan Adam da wayar da kai (CHRICED) Dakta Ibrahim M Zikirullahi ya bayyana cewa, Jahar Kano na kokari wajen tabbatar da an samu Cigaba mai dorewa a fannin lafiya ta bangare Samar da doka akan rage mace mace mata Masu juna biyu da kananan yara tun lokacin Tsohon Gwamna Rabiu Musa Kwankwaso a shekarar 2001.

Dakta Ibrahim ya bayyana haka a lokacin da yake ganawa da manema labarai da kuma kungiyoyi Masu zaman kan su kan Samar da hanyoyin magance matsalar yawan mace-mace mata Masu juna biyu da kananan yara ta Samar da dabaru don zantar da dokar haihuwa kyauta.

Kididiga na nuna cewa, jihar Kano na Cigaba da zama a sahu farko wajen samun yawan Mace -mace mata Masu juna biyu da kananan yara a kasar, Wanda haka ya zama barazana ga fannin lafiya a kasa.

Dakta Ibrahim ya Kara da cewa, rashin zartar da dokar haihuwa kyauta a asibitocin mu na Kara yawan mace-mace mata Masu juna biyu da kananan yara.

Hakazalika, zartar da dokar zai Kara bawa kananon asibitocin da ke a matakin farko Samar Samu kulawa tare da horar da likitoci da kuma Kara inganci aikin su .

Tabbas Gwamnoni da ake yi a Kano sunyi kokari wajen Samar da Dokar Wanda har yanzu wasu jahohin na matakin farko,sai dai zartar da dokar a jahar na zama tsaiko idan ka ga yadda kididiga ke nuna wa tun bayan kaddamar da dokar a watan mayu shekarar 2023.

PRNigeria Hausa

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 15 hours 30 minutes 12 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 17 hours 11 minutes 37 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com