Home General Gwamnatin Nijeriya tace zata kawo karshen wahalar Man Fetur a kasar

Gwamnatin Nijeriya tace zata kawo karshen wahalar Man Fetur a kasar

Ƙaramin Ministan Albarkatun Man Fetur, Heineken Lokpobiri ya ce daga yanzu zuwa ƙarshen mako man fetur zai wadata a ko’ina a faɗin ƙasar.

Ministan ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan ganawarsa da mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima a fadar shugaban ƙasar.

Ministan ya ce shugaban ƙasa ne ya buƙaci mataimakinsa ya kira taron na gaggawa domin sanin halin da ake ciki a game da batun man fetur.

A ranar Talata ne kamfanin NNPCL ya sanar da ƙarin farashin litar mai daga naira 617 zuwa naira 897.

“Abu mafi muhimmanci a yanzu shi ne akwai man, sannan muna da yaƙinin nan zuwa ƙarshen mako zai wadata a ko’ina a faɗin ƙasar nan.”

Ya ƙara da cewa farashin zai bambanta a wurare, “amma mun yi amannar cewa idan ya wadata, dole farashin zai ragu sosai.”

Ministan ta kuma bayyana cewa shugaban ƙasa ya damu da halin da ƴan Najeriya suke ciki, inda ya ce hakan ne ma ya sa ya umarci mataimakinsa ya kira taron domin tattaunawa da kuma neman mafita.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp