Home General Gwamnatin Kano ta dakatar da tsawaita wa’adin ma’aikata 4,000 da Ganduje ya...

Gwamnatin Kano ta dakatar da tsawaita wa’adin ma’aikata 4,000 da Ganduje ya yi

Aƙalla ma’aikan jihar Kano 4,000 da gwamnatin tsohon gwamnan Abdullahi Umar Ganduje ta tsawaita wa wa’adin aiki ne ake sa ran za su ritaya a ranar 1 ga Disamban 2024.

Gwamnatin jihar ta ce ta kammala bincike da tantace ma’aikatan, waɗanda aka yi wa ƙarin wa’adin aiki bayan sun kai shekara 35 suna aiki, ko kuma sun kai shekara 60 a duniya.

Ganduje ne ya assasa shirin tsawaita wa’adin aiki a jihar, inda ma’aikata za su iya cigaba da aiki har na tsawon shekara biyar bayan sun kai lokacin ritaya.

Bayan gwamna Abba Yusuf ya ɗare karagar mulki a ranar 29 ga Mayun 2023 ne ya soke wannan ƙudurin, sannan ya yi umarni a dawo da shekarun ritayar shekara 35 ana aiki ko kuma shekara 60 a rayuwa.

Da yake zantawa da manema labarai, Shugaban Ma’aikatan jihar, Abdullahi Musa ya ce bayan an soke ƙudurin ne, aka kafa kwamiti domin kididdige adadin ma’aikatan.

“Bayan bincike ne kwamitinmu ya gano cewa kusan ma’aikata 4,000 suke cikin wannan tsarin, amma za su yi ritaya a 1 ga Disamban 2024. Wannan na nufin a ƙarshen watan Satumba za su miƙa takardar ajiye aiki,” inji shi kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Sai dai Abdullahi Musa ya ƙara da cewa gwamnati ta shirye maye gurbin da za su bari bayan sun yi ritayar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp