Home General NERC ta ci tarar kamfanin AEDC kan tsauwala kuɗin wuta

NERC ta ci tarar kamfanin AEDC kan tsauwala kuɗin wuta

Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Najeriya (NERC) ta ci kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Abuja (AEDC) tarar Naira Biliyan 1.69 bisa laifin tsauwala wa abokan hulɗarsu kuɗin wuta

Gidan talbijin na Channels ya rawaito cewar tarar ta ta’allaka ne a kan rashin bin umarnin da hukumar ta bayar a baya na iyakance kiyasin lissafin kuɗi ga masu amfani da wutar lantarki.

Hukuncin, wanda aka zayyana a cikin takarda mai suna ‘Order NERC/2024/114’, wani ɓangare ne na umarnin hukumar na watan Satumba na shekarar 2024.

Umurnin mai kwanan watan Agusta 30, ya samu sa hannun mataimakin shugaban NERC Musiliu Oseni da kwamishinan shari’a da lasisi da bin doka, Dafe Akpeneye.

Tarar ta fito ne ta shafin intanet na NERC kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito.

Binciken da NERC ta yi kan tsarin biyan kudi na AEDC ya nuna cewa kamfanin tsalawa kwastomomi fiye da kima a tsakanin watan Janairu zuwa Satumba na 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp