Home General Tinubu ya kai ziyara Maiduguri don jajantawa al’umma iftila’in ambaliya

Tinubu ya kai ziyara Maiduguri don jajantawa al’umma iftila’in ambaliya

Shugaba Bola Tinubu ya kai ziyara birnin Maiduguri domin jajantawa al’ummar jihar Borno iftila’in ambaliyar da ya afka musu.

Ziyarar tasa na zuwa ne kwanaki shida bayan mummunar ambaliyar da birnin ya fuskanta wanda rabon a ga haka tun bayan shekara 30 da suka wuce.

Bayan isarsa birnin, kai-tsaye ya garzaya ɗaya daga cikin sansanonin da aka tsugunar da waɗanda lamarin ya ɗaiɗaita domin jajanta musu.

Tinubu ya yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta tallafawa mutanen.

“Ina son tabbatar muku da cewa za mu tallafa muku domin rage raɗadin da kuka shiga sakamakon wannan iftila’i,” in ji Tinubu.

Daga bisani, Tinubu ya ziyarci fadar Mai Martaba Shehun Borno, Alh Umar Garbai Ibn El-Kanemi tare da rakiyar gwamna Babagana Zulum domin jajantawa Basaraken kan al’amarin da ya faru.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp