Home General An samu raguwar hauhawar farashi a watan Agusta – NBS

An samu raguwar hauhawar farashi a watan Agusta – NBS

Hukumar kididdiga ta Najeriya (NBS) ta ce an samu raguwar hauhawar farashi a ƙasar daga kashi 33.40 a watan Yuni zuwa kashi 32.15 a watan Agusta.

A cewar wani rahoto da NBS ɗin ta fitar ranar Litinin, ta ce an samu raguwar ta kashi 32.15 ne a watan Agustan 2024, yayin da farashin abinci kuma ya kasance a kashi 37.52 a watan na Agusta.

“Alkaluman da muka tattara sun nuna cewa an samu raguwar kashi 1.25 idan aka kwatanta da n watan Yulin 2024,” in ji rahoton.

NBS ta ce farashin kayan abinci a watan Agustan 2024 ya kai kashi 37.52, idan aka kwatanta da adadin da aka samu a watan Agustan 2023 na kashi 29.34.

Ta ce an samu hauhawar farashin kayan abincin ne sakamakon tashin farashin kayayyaki kamar burodi da masara da hatsi da dawa da dankalin turawa da rogo da dabino da sauransu.

Hukumar ta ce farashin abinci a watan Agustan 2024 ya kasance a kashi 2.37 wanda ya nuna raguwa da kashi 0.10 idan aka kwatanta da adadin da aka samu a watan Yulin 2024 na kashi 2.47.

Ta ce za a iya danganta raguwar da faɗuwar farashin kayayyaki kamar sikari da ganyen shayi da man gyaɗa da madara da dawa ganyayyaki da sauransu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp